International sports

West Ham 1-2 Man Utd: Cristiano Ronaldo da Jesse Lingard sun ci kwallo

 

Cristiano Ronaldo

Manchester United ta je ta doke West Ham United da ci 2-1 a wasan mako na biyar a gasar Premier League ranar Lahadi.

Said Benrahma ne ya fara ci wa West Ham kwallo a minti na 30 da fara take tamaula, sai dai minti biyar tsakani Cristiano Ronaldo ya farke.

Kwallon da Ronaldo ya ci West Ham ya zama fili na 66 da ya zura kwallo a raga a tsakanin manyan gasar Turai biyar, tun bayan da ya fara buga wa Manchester United tamaula a 2003/04, yana kan gaba da Zlatan Ibrahimovic mai 64.

Haka kuma kwallo na hudu da ya ci wa United a wasa uku, bayan da ya koma Old Trafford a bana daga Juventus, har da wadda ya zura a biyu da ya zura a ragar Newcastle United a Premier League da dayan da ya ci Young Boys a gasar Champions League ranat Talata.

A minti na 89 Jesse Lingard ya ci wa Manchester United na biyu, watakila hakan ya wanke zuciyar magoya bayan United, bayan da shine ya yi kuskuren bayar da kwallo Young Boys ta ci United ta biyu ranar Talata a gasar Zakarun Turai.

Lingard ya zama na 47 da ya zura kwallo a ragar West Ham, kuma ya ci mata a lokacin da ya buga mata wasannin aro a bara, kuma West Ham ce kan gaba da take da yawan ‘yan wasan da suke buga mata wasa su ci mata kwallaye, idan sun barta su kuma zura mata kwallo a ragarta.

A cikin karin lokaci ne West Ham ta samu bugun daga kai sai mai tsaron raga, inda Mark Noble ya buga, sai dai golan United, David de Gea ya tare ta kasa shiga raga, kuma karon farko da ya buge fenariti tun cikin watan Afirilun 2016 a United da kuma tawagar Sifaniya.

Tun kafin ranar ta Lahadi an zura kwallo 40 a ragar De Gea a jere a bugun fenari da aka buga masa a kungiya da a Sifaniya.

Source: www.bbc.com

Ogyem Solomon

Solomon Ogyem – Media Entrepreneur | Journalist | Brand Ambassador Solomon Ogyem is a dynamic Ghanaian journalist and media entrepreneur currently based in South Africa. With a solid foundation in journalism, Solomon is a graduate of the OTEC School of Journalism and Communication Studies in Ghana and Oxbridge Academy in South Africa. He began his career as a reporter at OTEC 102.9 MHz in Kumasi, where he honed his skills in news reporting, community storytelling, and radio broadcasting. His passion for storytelling and dedication to the media industry led him to establish Press MltiMedia Company in South Africa—a growing platform committed to authentic African narratives and multimedia journalism. Solomon is the founder and owner of Thepressradio.com, a news portal focused on delivering credible, timely, and engaging stories across Ghana and Africa. He also owns Press Global Tickets, a service-driven venture in the travel and logistics space, providing reliable ticketing services. In addition to his media ventures, Solomon serves as a Brand Ambassador for Alabuga, a prominent Russian industrial company, representing their interests and expansion across Africa. He previously owned two notable websites—Ghanaweb.mobi and ShowbizAfrica.net—both of which contributed to entertainment and socio-political discussions within Ghana’s digital space. With a diverse background in media, digital journalism, and business, Solomon Ogyem is dedicated to telling impactful African stories, empowering youth through media, and building cross-continental media partnerships.

Related Articles

Back to top button