International sports

Real Madrid ta hau kan teburin La Liga bayan cin Cadiz

Minti 30 ana tsaka da wasa Karim Benzema ya fara ci wa Real Madrid kwallo 

Real Madrid ta je ta doke Cadiz da ci 3-0 a wasan mako na 31 a gasar La Liga da suka fafata ranar Laraba.

Minti 30 ana tsaka da wasa Karim Benzema ya fara ci wa Real Madrid kwallo a bugun daga kai sai mai tsaraon raga.

Minti uku tsakani Alvaro odriozola ya ci na biyu, saura minti biyar su tafi hutu Karim Benzema ya kara na uku, kuma na biyu da ya ci a wasan.

Da wannan Sakamakon Real Madrid ta koma ta daya a kan teburi da maki 70 iri daya da wanda Atletico keda shi.

Real ta samu wannan damar, bayan da ta yi nasara a kan Atletico a haduwar da suka yi, inda ta ci 2-1 a gida, sannan ta tashi 1-1 a Atletico.

Idan ba haka ba Atletico ta zura kwallo 57 aka zura mata 20, ita kuwa Real 56 ta zura a raga aka ci ta 24.

Sai dai ranar Alhamis Atletico Madrid za ta yi wasan mako na 31, inda za ta karbi bakuncin Huesca, wadda suka tashi 0-0 a wasan farko.

A dai ranar Alhamis Getafe za ta ziyarci Barcelona wadda ta lashe Copa del Rey na bana.

Barcelona wadda ta buga wasa 30 tana ta hudu a kan teburi da maki 65, Sevilla ce ta uku mai maki 67, bayan da ta yi karawa 32 a gasar bana.

Source: bbc.com

Ogyem Solomon

Solomon Ogyem – Media Entrepreneur | Journalist | Brand Ambassador Solomon Ogyem is a dynamic Ghanaian journalist and media entrepreneur currently based in South Africa. With a solid foundation in journalism, Solomon is a graduate of the OTEC School of Journalism and Communication Studies in Ghana and Oxbridge Academy in South Africa. He began his career as a reporter at OTEC 102.9 MHz in Kumasi, where he honed his skills in news reporting, community storytelling, and radio broadcasting. His passion for storytelling and dedication to the media industry led him to establish Press MltiMedia Company in South Africa—a growing platform committed to authentic African narratives and multimedia journalism. Solomon is the founder and owner of Thepressradio.com, a news portal focused on delivering credible, timely, and engaging stories across Ghana and Africa. He also owns Press Global Tickets, a service-driven venture in the travel and logistics space, providing reliable ticketing services. He previously owned two notable websites—Ghanaweb.mobi and ShowbizAfrica.net—both of which contributed to entertainment and socio-political discussions within Ghana’s digital space. With a diverse background in media, digital journalism, and business, Solomon Ogyem is dedicated to telling impactful African stories, empowering youth through media, and building cross-continental media partnerships.

Related Articles

Back to top button